Épisodes

  • Yadda Cire Darasin Lissafi Zai Taimakawa Dalibai Shiga Jami’a
    Oct 16 2025

    Send us a text

    Cire darasin Lissafi daga jerin wajibcin da ake buƙata domin samun shiga manyan makarantu ya samu karɓuwa daga wasu ɓangarori na dalibai da malamai. Wasu dalibai sun nuna farin ciki da wannan mataki, suna ganin zai sauƙaƙa musu damar samun shiga jami’a da sauran manyan makarantu ba tare da shan wahalar lissafi ba.


    Sai dai wasu masana sun bayyana cewa, duk da wannan sauƙin, ya kamata a yi taka-tsantsan saboda lissafi na taka muhimmiyar rawa wajen gina tunani da fahimtar ilimin fasaha, kimiyya da injiniya. Wannan ya sa ake tambaya ko cire lissafi daga wajabcin shiga manyan makarantu ba zai iya rage ingancin dalibai a nan gaba ba.


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Voir plus Voir moins
    19 min
  • Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
    Oct 14 2025

    Send us a text

    Shekara da shekaru kungiyar malaman jami’oi ASUU ta kwashe ta na gudanar da yajin aiki ba tare da samun biyan bukata ba.


    Irin wannan yajin aiki da kungiyar malaman ke shiga ya jefa dalibai da malaman da ma harkar ilimi cikin halin ni ‘yasu a Najeriya.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan wasu hanyoyin da kungiyar malaman ASUU za ta iya bi don warware matsalar ta ba tare da dogaro da gwamnatin tarayya ba.

    Voir plus Voir moins
    23 min
  • Kalubalen Da Ke Gaban Sabon Shugaban Hukumar Zabe Ta Kasa
    Oct 10 2025

    Send us a text

    A duk lokacin da a ka samu canjin shugabanci, hakan kan zo da kalubale da dama.


    Muƙamin shugabancin Hukumar Zabe ta kasa na daga cikin mukamai a Najeriya da 'yan kasa ke cece-kuce a kai.

    Ko wadanne irin Kalubale ne ke gaban sabon shugaban hukumar zabe ta kasa?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari akai.

    Voir plus Voir moins
    22 min
  • Abin Da Dokar Kasa Ta Ce Kan Nada Shugaban Hukumar Zabe
    Oct 9 2025

    Send us a text

    A tsarin mulkin Najeriya, an bai wa Shugaban Ƙasa ikon naɗa shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) tare da sauran mambobinta. Wannan iko yana daga cikin muhimman nauyukan da ke hannun shugaban ƙasa domin tabbatar da cewa ana gudanar da zaɓe cikin tsari, gaskiya da adalci.


    Sai dai, kafin wanda shugaban ƙasa ya naɗa ya fara aiki, dole ne a nemi amincewar Majalisar Dattawa, domin tabbatar da cewa wanda aka zaɓa ya cancanci rike wannan muhimmiyar kujera. Wannan tsari yana taimakawa wajen tabbatar da cewa hukumar zaɓe ta kasance mai zaman kanta, ba ta karkata ga wani ɓangare na siyasa ba, kuma tana iya gudanar da aikinta cikin gaskiya da amana.


    wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Voir plus Voir moins
    28 min
  • Tasirin Takardun Shaida Na Bogi Ga Rayuwar Al’umma
    Oct 7 2025

    Send us a text

    Takardun shaida na bogi na daya daga cikin matsaloli dake kara addabar Najeriya a fannoni da dama.


    A wasu lokuta ana samun mutane da ke amfani da takardun makaranta ko na ƙwarewa da ba su cancanta da su ba domin samun aiki, mukami, ko wasu fa’idodi da suka wajaba ne kawai ga waɗanda suka cancanta.

    Wannan dabi’a ta zama barazana ga ci gaban ƙasa da amincin al’umma gaba ɗaya, domin tana lalata tsarin ilimi, rage darajar masu gaskiya, da haifar da rashin inganci a wuraren aiki. Haka kuma, tana haifar da rashin amincewa tsakanin gwamnati da jama’a, da kuma tsakanin mutane da kansu.


    wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

    Voir plus Voir moins
    28 min
  • ‘Halin Kunci Ya Sa Muke Zama A Baca A Abuja’
    Oct 6 2025

    Send us a text

    Halin matsin tattalin arziki ya tilasta da yawa daga cikin mutane zama a bacoci a garin Abuja da wasu biranen Najeriya.


    Mutane a birane kamar Abuja da Legas Da Fatakwal na cikin halin matsi sakamakon rashin ingattaccen muhalli.

    Ko wannen irin rayuwa irin wadannan mutanen ke yi?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai a yau da ake bikin ranar muhalli ta duniya.

    Voir plus Voir moins
    27 min
  • Yadda Fasahar AI Ke Barazana Ga Sana’ar Masu Shagunan Daukar Hoto
    Oct 3 2025

    Send us a text

    A zamanin yau na fasahar zamani, musamman fasahar kirkirarriyar basir ta (AI), harkokin sana’o’i da dama suna fuskantar sauye-sauye masu girma. Daya daga cikin sana’o’in da ke cikin babban hadari shi ne sana’ar ɗaukar hoto musamman irin wadanda ke kashe makudan kudi wajen sayen kyamara da bude katafaren gidajen daukar hoto.


    A da, mutane kan je shagon daukar hoto domin samun hoto mai kyau na fasfo ko na bikin aure ko bikin suna, ko kuma kowane irin taron biki. Amma yanzu, manhajojin AI suna ba wa mutane damar kirkirar irin wadannan hotuna daga wayoyin su ko kwamfuta cikin mintuna kadan ba tare da zuwa shagon daukar hoto ba.

    Wannan yanayi na iya jefa masu shagunan daukar hoto cikin matsala ta rashin samun kudin shiga da kuma rasa sana’ar gaba ɗaya, muddin ba su bullo da sabbin dabarun jawo hankalin kwastomomi ba.


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba akai.

    Voir plus Voir moins
    23 min
  • Abin Da Dokar Kasa Ta Ce Kan Takarar Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan
    Oct 2 2025

    Send us a text

    Batun siyasar Najeriya ya sake ɗaukar hankali yayin da jam’iyyar PDP ta bayyana cewa tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, zai tsaya mata takarar shugaban ƙasa a 2027.
    Wannan batu ya tayar da muhawara mai zafi a tsakanin masana, da ‘yan siyasa da ma al’umma.


    Idan za a iya tunawa dai, an rantsar da tsohon shugaban ƙasan, har sau biyu: a karo na farko a shekarar 2010 bayan rasuwar tsohon shugaban kasa Umaru Musa Yar’adua, sannan kuma a karo na biyu a 2011 bayan lashe zaben da ya biyo baya.

    Amma abun tambayar a nan shine, shin ko me dokar kasa ta bayyana kan takarar tsohon shugaban kasan bayan rantsar dashi har sau biyu kan karagar mulki?
    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.


    wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Voir plus Voir moins
    27 min